Kotu ta umarci INEC ta maye gurbin Shekarau da Rufa’i Hanga
Kotun Ƙolin Najeriya ta umarci hukumar zaɓen ƙasar ta maye gurbin sunan Mallam Ibrahim Shekarau da na Rufa’i Hanga na jamiyyar NNPP, a matsayin sanatan mazabar Kano ta tsakiya.
A hukuncin da mai shari’a Justice Uwani Abba-Aji ta yanke yau Juma’a, kotun ta amince da hukuncin da kotun ɗaukaka kara ta yi a baya, inda ta umarci INEC ta amince da Rufa’i Hanga a matsayin dan takarar jam’iyyar NNPP na mazaɓar a zaɓen ranar 25 ga watan Fabarairu, 2023.
Ita dai INEC ta ayyana shekarau a matsayin wanda ya ci zaben, kasancewar ta ki yarda da janye sunansa da ya yi a matsayin dantakarar NNPP tun da farko bayan da hukumar ta ce lokacin sauya dan takara ya wuce.
Jam’iyyar NNPP ta maye gurbin Shekarau a matsayin dan takara bayan da tsohon gwamnan Kanon ya fice daga jam’iyyar ya koma PDP.